
*Media Adverts*
*Media/News Campany Ng Ltd.*
*Dadumi Dumin Sa:Alummar Talata Mafara Da Anka sunce koda za a chanza wakili to lalle sun gama Zabi*
*Tawaga Mai karfin Gaske karkashin Jagoranci Alhaji shafi’u Buhari(Big Man) da Hon Mustapha Sabitu(Dan America) Sunyi ganawar sirri Da Fitattacen dan siyasar nan HON•ABUBAKAR MUHAMMAD BARMO(Dan Galadiman Mafara)*
*Sakataren din din a ofishin Mai Girma Gwamna*
*Ziyarar ta samu rakiyar Manyan mutane ,matasa maza da mata Domin tattauna muhimman bayanai da Mai Girma Dan Galadiman mafara.Wakilin Ma’aikatar yada labarai ta Media Adverts📡(Ibrahim Abdullahi Bernat)ya rahoto cewa Tawagar ta samu ganawa da mai Girma Sakataren Din din a Ofishin mai Girma Gwamnan jihar zamfara A gidan sa dake garin talata mafara*
*Yayin da jagoran da ya jagoranci wannan ziyara yake Jawabi ya bayyana cewa Alummar garin talata mafara suna alfahari salon irin taimakon Dan galadiman mafara a karkashin jagorancin Gwamnatin mai girma Gwamnan jihar zamfara DR BELLO MATAWALLEN MARADUN(Shattiman Sokoto)*
*Inda yakara dacewa mai girma HON ABUBAKAR MUSA MAI NAIRA(Sadaukin Mafara)Mai Baiwa Mai Girma Gwamnan jihar zamfara shawara yace jagorane mai kokarin Ganin Alummar sa ba a yaudare su ba kuma ba a yimasu mulki Yan na iyaba,Hakane yasa wannan tawaga ta matasa Tazo domin Nuna Goyon bayan ta Ga wannan haziki kuma mai taimakon alumma*
*Duk Wanda yasan labarin Abubakar Muhammad Barmo yasan dacewa bakaramin Alkhairi bane samun sa garin Talata mafara,Domin kuwa ya nuna shi mutun ne mai Nagarta kuma Amintacce hakan ne ya janyo Yaro da babban zakaji suna ambaton sa da alheri*
*Dan Galadiman Mafara,Zai zo a jerin mutane na farko masu bada Gudunmuwa da tallafi ga alumma wajen gyaran Ilimi,Samarda jari ga matasa,samarda ingantattun Gine gine A ciki da wajen garin Domin Alumma su samu mazauni,Maluman Addini Tabbas yana basu kulawa da duk wani dan siyasa dake garin Da kuma baiwa alumma muhimmanci wanda hakan babbar nasarace*
*Daga Karshe tawagar ta Nuna Goyon bayanta Dari bisa dari ga jagoran tareda bada tabbacin suna tare dashi*
*Media Adverts Correspondent Zamfara state……..*

